in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin a shirye take ta tura kwararru DRC bayan barkewar cutar Ebola
2018-05-21 10:00:08 cri
Wani jami'in kiwon lafiyar kasar Sin ya ce kasarsa ta lura da halin da ake ciki game da barkewar annobar cutar Ebola a jamhuriyar demokaradiyyar Kongo (DRC), kuma a shirye take ta aike da tawagar kwararrun masana kiwon lafiya, idan an bukaci hakan.

Ma Xiaowei, shugaban kwamitin lafiyar kasar Sin, kana jagoran tawagar kasar Sin da za su halarci taron kiwon lafiya na duniya (WHA) wanda za'a bude a Geneva a ranar Litinin. Ya bayyana a taron manema labarai cewa, Sin ta damu matuka game da halin da ake ciki na barkewar annobar cutar Ebola a DRC.

Alkaluma na baya bayan nan da mahukuntan DRC suka fitar ya nuna cewa, ya zuwa ranar Asabar adadin mutanen da aka tabbatar sun kamu da cutar sun karu daga 17 zuwa 21.

Ma ya ce, a shekarar 2014 a lokacin da cutar Ebola ta barke a yammacin Afrika, gwamnatin kasar Sin da al'ummar Sin sun kai daukin gaggawa, Sin ta aike da kwararru da masana kiwon lafiya zuwa kasashen yammacin Afrika don bada taimako wajen shawo kan annobar cutar Ebola.

Ya kara da cewa, kasar Sin tana bibiyar yadda cutar Ebola ta barke a halin yanzu a DRC, ya ce idan an bukaci taimako, gwamnatin Sin da al'ummar Sinawa za su tura kwararru domin bada taimako. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China