in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Nijeriya zai gana da takwaransa na Amurka game da tattalin arziki da tsaro
2018-04-28 16:17:49 cri
Shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari, zai kai ziyara Amurka a yau Asabar, inda zai gana da shugaban kasar Donald Trump, game da batutuwan da suka shafi tattalin arziki da tsaro.

Kakakin Shugaban kasar Femi Adeshina ne ya bayyana haka a jiya Juma'a, inda ya ce shugabannin biyu za su gana game da hanyoyin inganta dangantaka a tsakanin kasashensu da kuma batutuwan da suke mayar da hankali kai da suka hada da habaka tattakin arziki da yaki da ta'addanci da sauran barazanar tsaro.

Femi Adeshina, ya ce Shugaba Buhari zai kai ziyarar aiki ne bisa gayyatar da Shugaba Trump ya yi masa.

Muhammadu Buhari zai bar Abuja babban birnin kasar ne a yau Asabar, inda kuma zai gana da Shugaba Trump a yau din.

Kakakin Shugaban ya ce, an kuma shirya wasu taruka tsakanin manyan jami'an gwamnatin Nijeriya da shugabannin manyan kamfanonin Amurka a bangarorin aikin gona da sufurin jiragen sama da kuma sufuri baki daya.

Ya ce an shirya ganawa tsakanin jami'an Nijerya da na Boeing, Kamfanin kera jirgin sama mafi girma a duniya, game da aikin kera jirgin sama mallakar Nijeriya. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China