Wata sanarwa da Kwamishinan yada labaran jihar, Ahmad Sajoh ya fitar, ta ce an kwantar da mutanen 56 da suka jikkata a asibiti, yana mai cewa 'yan kunar bakin wake biyu ne suka kai hare-haren.
A cewarsa, bam na farko ya tashi ne a wani masallaci, yayin da maharin na biyu, ya ta da nashi a wata kasuwar gwanjo dake kusa da masallacin da aka kai wa hari na farko.
Ko cikin watan Nuwamban bara, a kalla mutane 50 sun mutu sanadiyyar wani harin da aka kai wani masallaci a garin na Mubi.
MDD ta ruwaito cewa, tun daga shekarar 2009, kungiyar 'yan ta'adda ta Boko Haram, ta yi sanadin mutuwar mutane sama da 20,000. (Fa'iza Mustapha)