in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Congo Kinshasa ta sanar da kawar da Ebola
2017-07-02 13:00:45 cri
Oly Ilunga Kalenga, ministan lafiya na jamhuriyar Congo Kinshasa, ya sanar a jiya Asabar cewa, an riga an kawo karshen annobar Ebola a kasar. Haka kuma jami'in ya nuna godiya ga gwamnatin kasar Sin kan tallafin da ta baiwa kasarsa.

A wajen taron manema labaru da ya gudana a jiyan, mista Kalenga ya ce, cikin kwanaki 42 da suka wuce, ba a gano karin mutum ko daya da ya kamu da cutar Ebola a kasar ba. Da ma hukumar lafiya ta duniya ta kayyade cewa, idan ba a samu karin wasu mutanen da suka kamu da cutar cikin kwanaki 42 a jere ba, to, za a iya sanar da kawo karshen annobar.

A cewar jami'in, annobar Ebola da ta barke a Congo Kinshasa a wannan karo, ta yi sanadiyyar mutuwar mutane 4. A madadin kasarsa, jami'in ya nuna godiya ga kungiyoyin kasa da kasa, gami da gwamnatin kasar Sin, wadanda suka kai dauki ga jama'ar kasarsa.

An fara gano barkewar annobar Ebola a kasar Congo Kinshasa a ranar 12 ga watan Mayun bana, wanda ya kasance karo na 8 da kasar ta sha fama da cutar Ebola tun daga shekarar 1976. Bayan da aka sanar da barkewar cutar Ebola a kasar a wannan karo, gwamnatin kasar Sin ta baiwa Congo Kinshasa taimakon dalar Amurka dubu 200, da kuma sauran wasu kayayyakin da za a iya amfani da su wajen baiwa mutane kariya daga kamuwa da kwayoyin cutar Ebola.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China