in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan kasar Sin ya ce babu wanda zai yi nasara a takaddamar ciniki
2018-04-26 21:36:54 cri
Yau Alhamis, a birnin Beijing, firaministan kasar Sin Li Keqiang ya gana da sakatariyar sufuri ta kasar Amurka, Elaine L. Chao, inda ya bayyana cewa, babu wanda zai yi nasara a takaddamar da ake yi tsakanin Sin da Amurka, kana, kofar kasar Sin a bude take wajen yin shawarwari.

Li ya nuna cewa, takaddamar cinikayya da ake yi, zai yi mummunan tasiri ga farfadowar tattalin arzikin duniya, kana, zama a tattauna ita ce hanya daya tilo da za'a iya bi wajen warware takaddamar. Kasar Sin za ta kara aiwatar da manufar yin gyare-gyare a gida da bude kofarta ga kasashen waje, haka kuma tana fatan kasashe daban-daban za su ci gajiyar wannan manufa. (Murtala Zhang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China