Yanayin damina na bana ya tsawaita a kasar Kenya, kuma ana ruwan sama mai karfi a wurare da dama a kasar, wanda hakan ke gurgunta zirga-zirga cikin wasu unguwannin dake babban birnin kasar, wato Nairobi da kuma a birnin Mombasa.
Babban sakataren kungiyar Red Cross ta kasar Kenya ya bayyana cewa, a kalla kananan hukumomi guda 32, dake cikin kananan hukumomin kasar Kenya guda 47 suna fama da matsalolin ambaliyar ruwa. (Maryam)