in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ambariyar ruwa a Kenya ta sanya mutane sama da dubu 210 rasa gidajensu
2018-04-26 11:07:58 cri
Kungiyar agaji ta red cross ta kasar Kenya, ta bayyana a jiya Laraba cewa, sakamakon yawan ruwan da aka yi tun farkon watan Maris, an samu bala'in ambariyar ruwa a yankuna da dama na kasar, kuma ya zuwa yanzu mutane sama da dubu 210 sun rasa gidajensu.

A cikin sanarwar da kungiyar ta bayar, an ce yankunan da suka fi fama da bala'in sun hada da Nairobi, babban birnin kasar, da Kisumu da Nourke dake yammacin kasar, da Kirifi da Tana dake gabashin kasar, da Marcueni da wasu gundumomin dake kudancin kasar, da kuma wasu gundumomin dake arewacin kasar.

Sanarwar ta ce, bala'in ambariyar ruwa ya lalata gidajen fararen hula da gandun noma da dama, kana an rushe wasu manyan kayayyakin more rayuwa, ciki har da hanyoyin mota, baya ga rasuwar dabbobin gida da yawa da hakan ya haifar.

Baya ga haka, sanarwar ta ce, kungiyar ba da agaji ta red cross ta kasar, ta riga ta aika da ma'aikata zuwa yankunan dake fama da bala'in, don gudanar da ayyukan ceto, da kuma samar da hidimar kiwon lafiya. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China