in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata a inganta zaman lafiya a zirin Koriya, in ji Li Keqiang
2018-05-09 13:56:14 cri
A safiyar yau Laraba, firaministan kasar Sin Li Keqiang, ya bayyana a yayin taron ganawa tsakanin shugabannin Sin, da Japan da Koriya ta Kudu cewa, ya kamata sassan su ci gaba da gudanar da shawarwari, domin warware sabanin dake tsakaninsu, kuma kasar Sin tana goyon bayan kasar Koriya ta Arewa da kasar Koriya ta Kudu, a fannin kyautata dangantakar dake tsakaninsu, tana taya su murnar cimma nasarar ganawar shugabanninsu a karo na uku, kuma tana fatan za a gudanar da ganawar shugaban kasar Amurka da na kasar Koriya ta Arewa cikin nasara.

Bugu da kari, Li Keqiang ya ce, kasar Sin tana goyon bayan bangarorin da abun ya shafa, da su karfafa shawarwari tsakaninsu domin warware sabani tun daga tushe, da kuma samun ci gaba a yunkurin warware matsalar zirin Koriya ta hanyar siyasa, da kafa tsarin shimfida zaman lafiya a zirin Koriya, ta yadda za a tabbatar da zaman lafiyar dindindin a yankin baki daya. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China