in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Koriya ta kudu zai ziyarci Amurka gabanin ganawar Shugaba Trump da Shugaba Kim na Koriya ta arewa
2018-05-05 15:54:25 cri
Shugaban Amurka Donald Trump, zai karbi bakuncin takwaransa na Koriya ta kudu Moon Jae-in a ranar 22 ga wannan watan. Ziyarar za ta zo ne gabanin ganawar da aka shirya yi tsakanin Shugaba Trump da Shugaban Koriya ta arewa kim Jong Un.

Sanarwar da Fadar White House ta fitar ta ruwaito cewa, shugabannin biyu wato Trump da Moon, za su tattauna ne kan ganawar dake tafe tsakanin Shugaban Amurkar da na Koriyar ta arewa.

Ziyarar ta Shugaba Moon, ta biyo bayan ganawarsa da shugaba Kim a ranar 27 ga watan Afrilun da ya gabata, inda shugabannin biyu suka tabbatar da burinsu na kawar da makaman nukiliya baki daya daga zirin Koriya.

Ana sa ran Donald Trump zai gana da Kim Jung Un a cikin wannan watan ko kuma farkon watan Yuni. Trump ya shaidawa manema labarai a jiya cewa, tuni aka sanya ranar da Amurka da Koriya ta arewa za su tattauna a karon farko, kuma nan bada dadewa ba za a sanar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China