in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojojin Najeriya sun lalata wani sansani na Boko Haram a jihar Borno
2018-04-24 09:21:23 cri
Mai magana da yawun rundunar sojojin tarayyar Najeriya dake aiki a jihar Borno Onyema Nwachukwu, ya ce jami'an sojin kasar sun lalata wani sansani da mayakan Boko Haram ke amfani da shi wajen samar da horo a jihar ta Borno dake arewa maso gabashin kasar.

Onyema Nwachukwu ya ce sojojin sun cimma wannan nasara ne, yayin wani aikin sintiri da suka gudanar a yankin Benisheikh dake jihar ta Borno. Kaza lika sojojin sun hallaka wani mayakin kungiyar daya, tare da kubutar da wani mutum guda da kungiyar ke tsare da shi. Jami'in ya ce sojojin sun samu bayanan sirri da suka taimaka masu wajen gano sansanin, a wani bangare na yunkurin da suke ci gaba da yi na raba daukacin jihar ta Borno da ayyukan 'yan ta'adda na Boko Haram.

Rahotanni sun bayyana cewa sai da sojojin suka yi musayar wuta da mayakan kungiyar kafin su kai ga cin lagon su. (Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China