in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Morocco da Nijer sun kulla yarjejeniyoyin karfafa dangantaka
2017-12-27 09:45:33 cri
A jiya Talata kasashen Morocco da Nijer suka rattaba hannu kan wasu yarjejeniyoyi 16 da nufin karfafa dangantakar dake tsakanin kasashen biyu, kamar yadda shafin intanet na ma'aikatar harkokin wajen Morocco ya wallafa.

An kulla yarjejeniyoyin ne a lokacin gudanar da taron hadin gwiwar kyautata mu'amala na Morocco-Nijer karo na 4, wanda ministan harkokin wajen Morocco Nasser Bourita, da takwaransa na Nijer Ibrahim Yacoubou suka jagoranta.

Yarjejeniyar ta shafi bangarori da dama, da suka hada da tattalin arziki, sufuri, kiwon lafiya, shari'a, yawon bude ido da raya al'adu.

Da yake jawabi a lokacin ganawar, Bourita ya yaba da irin rawar da jamhuriyar Nijer ta taka wajen kokarin wanzar da zaman lafiya da tsaron yankin Sahel, ya kuma bayyana irin karuwar kalubalen tsaro dake addabar yankin na Sahel.

Yacoubou ya yabawa Morocco bisa yadda take ci gaba da nuna goyon baya ga Nijer, kana ya jaddada muhimmancin hadin gwiwar dake tsakanin kasashen biyu da cewa tamkar abin koyi ne a nahiyar Afrika, kuma bangare ne na hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa.

Haka zalika ya yabawa kasar Morocco sakamakon matakin da ta dauka na sake zama mamba a kungiyar tarayyar Afrika (AU), ya ce wannan babban abin alfahari ne ga kungiyar ta Afrika.

Ministan harkokin wajen na Nijer ya kuma nuna goyon bayansa ga bukatar da kasar Morocco ta nema na shiga kungiyar ECOWAS. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China