in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Li Keqiang: kasar Sin ba za ta yunkura kara girmanta ba har abada
2018-03-20 13:04:20 cri

Yau Talata a nan Beijing, Li Keqiang ya ce, kasar Sin ba za ta yunkura kara girmanta ba har abada, za ta maida hankali ne kan daidaita harkokinta.

Li ya kara da cewa, kasar Sin, kasa ce mai tasowa. Ba ta da yunkurin kara girmanta. Koda a nan gaba ta bunkasa, amma ba za ta ci zalin sauran kasashen duniya ba. Tana son raya hulda a tsakaninta da sauran kasashe bisa ka'idar girmama juna da yin zaman daidai wa daida da cin moriyar juna, a kokarin raya al'umma mai kyakkyawar makoma ga dukkan bil'Adama.

Ya ci gaba da cewa, kasar Sin tana kiyaye cikakkun yankunanta, ba kuma za ta yarda da raba wani yanki daga jikinta ba. Duk da haka, ba za ta mamaye sauran yankuna ba. Kasar Sin tana bin hanyar samun ci gaba ne ta hanyar lumana. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China