Mahamat ya yi wannan tsokaci ne a lokacin ganawa da sabon firaiministan kasar Habasha, Abiy Ahmed.
Ganawar ta Ahmed da Mahamat ita ce ta farko a hukumance, tun bayan da sabon firaiministan ya kama aiki a ranar Litinin bayan da ya karbi aiki daga hannun tsahon firaiministan kasar Habashan Hailemariam Desalegn, wanda ya yi murabus daga aiki a ranar 15 ga watan Fabrairu sakamakon zanga zangar kin jinin gwamnatin da aka gudanar a sassan kasar.
Mahamat ya yabawa kokarin gwamnatin Habasha bisa rawar da take takawa wajen tabbatar da zaman lafiya, tsaro, da batutuwan da suka shafi cigaban shiyyar.(Ahmad Fagam)