in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta yi maraba da sauyin shugabancin Habasha cikin ruwan sanyi
2018-04-03 09:37:24 cri
Shugaban kungiyar tarayyar Afrika (AU), Moussa Faki Mahamat, yayi maraba da sauyin gwamnatin kasar Habasha cikin kwanciyar hankali, kana ya jaddada aniyar yin aiki tare da sabon firaministan kasar Abiy Ahmed, wajen aiwatar da muhimman ayyukan gina kasar.

Mahamat, ya taya Abiy Ahmed murnar tabbatar da shi a matsayin sabon firaministan kasar ta gabashin Afrika a ranar Litinin, inda kuma ya yaba da yadda aka sauya shugabancin kasar cikin lumana, kana ya bayyana matakin da cewa alamu ne dake nuna samun kyautatuwar siyasa a kasar Habashan.

Ahmed, wanda ya samu amincewar kafatanin 'yan majalisar wakilan kasar Habashan a matsayin sabon firaministan kasar a ranar Litinin, ya karbi ragamar shugabancin tun a jiya Litinin daga hannun tsohon firaministan kasar Hailemariam Desalegn, wanda ya yi murabus a ranar 15 ga watan Fabrairu bayan zanga-zanagar data barke a sassan kasar don kin jinin gwamnati.

Shugaban na AU ya yabawa tsohon firaiministan kasar bisa irin gudumowar da ya bayar wajen cigaban kasar Habasha da nahiyar Afrika baki daya.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China