Al'ummar Sin sun kara amincewa da yadda ake kare ikon mallakar fasaha a kasar
Yau Alhamis 26 ga wata, rana ce ta kare ikon mallakar fasaha ta kasa da kasa. Wannan shi ne karo na farko da hukumar kula da harkokin kare ikon mallakar fasaha ta kasar Sin ta kaddamar da rahoton bincike kan yadda al'ummar kasar suka nuna amincewa da harkokin kare ikon mallakar fasaha, inda aka nuna cewa, al'ummar Sin sun kara amincewa da yadda ake kare ikon mallakar fasaha a kasar, kana kuma sun fi amincewa da yadda kamfanoni masu jarin waje da kuma masu jarin gida da waje suke kare ikon mallakar fasaha, kamar yadda kamfanoni masu zaman kansu a kasar. (Tasallah Yuan)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku