in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta kara yawan kudaden da take kashewa a makarantun reno
2018-01-23 20:12:33 cri
Ministan Ilimi na kasar Sin Chen Baosheng ya bayyana kudurin kasarsa na kara yawan kudaden da ake kashewa da ma tallafin da ake baiwa makarantun reno.

Ministan wanda ya bayyana hakan Talatar nan yayin taron karawa juna sani kan harkokin ilimi na kasa, ya ce ma'aikatar ilimin za ta tsara yawan kudaden da gwamnatin za ta kashe kan makarantun renon kasar da kuma rangwamen da za a yiwa yaran dake karatu a makarantun reno masu zaman kansu.

Ya ce, za kuma a dauki managartan matakai game da biyan malamai albashi da abubuwan karfafa gwiwa a kan kari, da kuma kara takardun kwarewarsu na aiki.

Ministan ya ce gwamnati za ta karfafa tare da taimakawa makarantun reno masu zaman kansu da suka samar da hidima mai rangwame sannan suka kashe kudade wajen gina sabbin makarantun da fadada wadanda ake da su a yankunan karkarar kasar, da yankuna marasa ci gaba, da wurare da yankunan da ake da matukar bukatar makarantun sakamakon sassauta manufar kayyade iyali da gwamnati ta yi. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China