in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar OPCW ta kara shiga Duma don binciken zargin hari da makamai masu guba
2018-04-26 10:42:03 cri
Hukumar haramta amfani da makamai masu guba ta kasa da kasa OPCW, ta bayar da sanarwa a jiya Laraba cewa, tawagar bincikenta ta kara shiga garin Duma na kasar Syria, don gudanar da bincike game da zargin da ake yiwa gwamnatin kasar da kaddamar da hari da makamai masu guba a yankin.

Sanarwar ta ce, bayan binciken da kungiyar ta yi a Duma a ranar 21 ga watan nan, a ranar 25 ga wata ta kara shiga garin, tare kuma da kai ziyara wani wurin na daban. An ce, za a debe burbushin shaidu da kwararru tawagar suka samu zuwa Rijswijk na lardin kudancin Holland, don a yi nazari a dakin gwaji da kungiyar OPCW ta amince da shi. Kaza lika kuma jami'an tsaron MDD, da gwamnatin Syria da kuma 'yan sandan Rasha sun ba da tabbaci ga tsaron tawagar jami'an dake aiki a Duma.

Baya ga haka, sanarwar ta ce, tawagar kasar Rasha ta sanarwa hukumar OPCW da cewa, za a shirya wani taro a ranar 27 ga wata a Hague dake lardin kudancin Holland, inda wasu 'yan kasar Syria za su bada shaidu game da zargin kai hari da makamai masu guba a Duma. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China