in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manzon musamman na Sin kan batun Syria: Hanyar siyasa ce kacal za ta dace da daidaita batun Syria
2018-04-23 10:57:29 cri
Manzon musamman na kasar Sin kan batun Syria Xie Xiaoyan wanda yake ziyarar aiki a kasar Masar, ya bayyana wa 'yan jarida a ranar 22 ga wata cewa, a halin yanzu, ya kamata bangarori daban daban da abin ya shafa su dau matakan sassauta halin da ake ciki a Syria.

Xie Xiaoyan ya yi nuni da cewa, hanyar siyasa ce kadai ta dace a bi wajen daidaita batun Syria. Ya kuma kamata kasa da kasa su maida hankali ga bukatu, da fatan jama'ar kasar Syria. Su kuma kara kokari wajen gudanar da shawarwari na shimfida zaman lafiya, da sa kaimi ga bangarori daban daban wajen komawa shawarwarin warware matsalar kasar.

Game da batun makamai masu guba da aka yi zargin gwamnatin kasar da amfani da su kan fararen hula a Syria, Xie Xiaoyan ya yi nuni da cewa, ya kamata a yi bincike kan batun cikin adalci a dukkan fannoni. Ya ce, ya kamata MDD ta nada ma'aikatan binciken, kuma ya dace su fito daga sassa daban daban. Kana a samu cikakkun shaidu kafin a gabatar da sakamakon binciken. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China