in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen Larabawa sun yi kira da yin bincike kan batun yin amfani da makamai masu guba a kasar Syria
2018-04-16 10:57:45 cri
Shugabannin kasashen Larabawa sun yi kira ga kasashen duniya da su kafa wani rukunin bincike mai zaman kansa domin yin bincike kan batun yadda aka yi amfani da makamai masu guba a kasar Syria.

Shugabannin sun yi kiran ne yayin taron koli na kawancen kasashen Larabawa na yini daya da aka yi jiya Lahadi a birnin Zahran dake gabashin Saudiyya.

Wata sanarwar da taron ya fitar ta ce, kasashen sun lura da matakan da kasashen yamma ke dauka a kasar Syria. Kuma sun yi Allah wadai da amfani da makamai masu guba kan jama'ar kasar. Sanarwar ta kuma nanata muhimmancin warware matsalar Syria a siyasance, kana ta yi kira ga duk sojojin kasashen waje dake Syria da su janye daga kasar, don kiyaye ikon mulkin kai da cikakken yankunan kasar Syria. (Bilkisu Xin)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China