in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakatare Janar na MDD ya yi kira da hada hannu wajen tabbatar da zaman lafiya a duniya
2018-04-25 11:30:38 cri

Sakatare Janar na MDD Antonio Guterres, ya yi kira da a hada hannu ga yunkurin taimakawa gwamnatocin kasashen duniya da al'ummominsu wajen samawa da tabbatar da dorewar zaman lafiya.

Da yake jawabi ga taron majalisar kan samar da zaman lafiya da tabbatar da dorewarsa, Antonio Guterres ya ce mataki da yanayin kalubalen da ake fuskanta, na bukatar kyakkyawan hadin gwiwa tsakanin masu ruwa da tsaki, bisa la'akari da muhimman batutuwa da manufofin da kasa ke ba fifiko.

A cewarsa, wadanan masu ruwa da tsaki sun hada da gwamnatoci da MDD da sauran hukumomin kasa da kasa da kungiyoyin yankuna da cibiyoyin harkokin kudi na kasa da kasa da kungiyoyin al'umma da na mata da matasa da kuma bangarori masu zaman kansu. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China