in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sakatare janar na MDD ya yi maraba da nada firaministan Guinea-Bissau
2018-04-18 10:32:47 cri
Babban sakataren MDD Antonio Guterres ya ce ya yi maraba da nada Aristides Gomes a matsayin sabon firaministan kasar Guinea-Bissau, da kuma sanarwar da aka bayar na shirya zaben majalisar dokokin kasar a ranar 18 ga watan Nuwamba 2018.

Stephane Dujarric, kakakin sakatare janar na MDD ya ce, mista Guterres ya nuna gamsuwa da salon shugabancin shugaban kasar Jose Mario Vaz, da kuma yadda manyan jam'iyyun siyasar kasar ke tafiyar da harkokinsu.

Sanarwar ta ce, babban jami'in MDDr ya bukaci dukkan bangarorin kasar da su hada kai wajen kaiwa muhimmin mataki na gaba, da suka hada da kafa gwamnatin hadin kan kasa, da sake bude majalisar dokokin kasar, da kuma aiwatar da ragowar yarjejeniyar da aka cimma ta Conakry.

Guterres ya ce, MDD za ta ci gaba da yin aiki tare da kungiyoyin shiyya wajen tallafawa sake gina zaman lafiya da kwanciyar hankali da kuma mara baya ga dukkan kokarin ci gaban kasar ta Guinea-Bissau. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China