in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Libya ta rufe aikin rejistar masu zabe 'yan kasar dake kasashen waje
2018-04-02 10:35:43 cri
Hukumar zaben kasar Libya ta sanar a Jiya Lahadi cewa, ta rufe aikin rejistar masu kada kuri'a 'yan kasar dake zaune a kasashen waje gabanin fara manyan zabukan kasar dake tafe.

Hukumar zaben kasar ta sanarwa dukkan 'yan kasar dake zaune a kasashen ketare cewa ya zuwa ranar 31 ga watan Maris na shekarar 2018, an rufe aikin rejistar masu kada kuri'ar dake zaune a kasashen waje, inda kawo yanzu hukumar ta yi rejistar kimanin mutane 6630.

Sanarwar tace an yi rejistar ne ta hanyar ofisoshin jakadancin kasar Libyan dake kasashen waje, wanda a halin yanzu an rufe aikin.

Hukumar tace, an kawo karshen aiki rejistar ne wanda aka fara shi a ranar 6 ga watan Disambar shekarar 2017, inda hukumar ta taya murna ga dukkan masu zabe dake kishin kasarsu wajen aza tubalin tabbatar da zaman lafiya da cigaban kasar.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China