in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar FIFA na duba yiwuwar dage haramcin buga wasa da ta yi wa filayen wasan Libya
2018-04-04 13:13:53 cri
Wani ayarin manyan jami'an hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA, sun isa Tripoli babban birnin Libya a jiya Talata,domin duba yuwar dage haramcin buga wasa da ya kai shekaru 5 da aka yi wa filayen wasan kasar.

A cewar kakakin hukumar kwallon kafa ta Libya, Fatih Halbus, ayarin jami'an FIFA sun isa kasar inda za su yi ziyarar yini 3, don hada cikakken rahoton kan yanayin tsaro da na kayaki a filayen wasan kasar, da nufin dage haramcin buga wasan kungiyoyin kasashen waje a filayen wasan da aka yi a shekarar 2013.

Kakakin ya tabbatar da cewa, ziyarar wani bangare ne na goyon bayan da hukumar FIFA ke ba hukumar kwallon kafa ta kasar.

Tun a shekarar 2013, FIFA ta haramta gudanar da wasanni da suka shafi kasashen waje a filayen wasan Libya saboda tabarbarewar tsaro a kasar. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China