in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin wajen Afrika ta kudu ya bukaci a kwantar da hankali game da sabon tsarin filaye na kasar
2018-03-05 10:21:33 cri
Ministan harkokin wajen Afrika ta kudu Lindiwe Sisulu, ya buakaci al'ummomin kasashen waje kada su tada hankalinsu game da sauye-sauyen tsarin filaye da kasar ta gabatar.

Da yake mayar da martani a jiya Lahadi, game da tsokacin da ake kan sabon tsarin majalisar dokokin kasar na rabon filaye, Lindiwe Sisulu, ya ce babu bukatar a tada hankali ko fargaba, yana mai cewa dole ne a mutunta tsare-tsaren majalisar.

Ya ce al'ummomin kasashen waje sun taka muhimmiyar rawa wajen yaki da wariyar launin fata da dukkan wasu banbance-banbancen da ya kunsa, Inda ya ce suna bukatar su ci gaba da mara musu baya ga kokarin da suke na kawar da wariyar launin fata.

A baya-bayan nan ne majalisar dokokin kasar ta amince da kudurin gyara wani bangare na dokar da ta bada damar kwace filaye ba tare da biyan diyya ba. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China