in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An dage sauraron shari'ar cin hanci da ake wa tsohon shugaban Afrika ta kudu
2018-04-07 12:01:33 cri
Babbar kotun Durban na kasar Afrika ta kudu, ta dage sauraron shari'ar da take yi wa tsohon shugaban Afrika ta kudu Jacob Zuma, zuwa ranar 8 ga watan Yuni mai zuwa.

Lauyoyin gwamnatin kasar da na wanda ake tuhuma, sun amince da neman dage sauraron shari'ar zuwa ranar 8 ga watan Yuni, wanda ya zo mintuna kalilan bayan Jacob Zuma ya gurfana na wani dan lokaci a gaban kotun, domin fuskantar tuhume-tuhume 16 da ake masa wadanda ke da nasaba da cin hanci da rashawa.

Jacob Zuma ya gabatar da jawabi ga dubban magoya bayansa da suka taro a wajen kotun, inda ya ce musu ba za a taba tabbatar da tuhume-tuhumen da ake masa ba.

Sai dai, jam'iyya mai mulkin kasar ANC ta kauracewa goyon bayan Zuma, tana mai cewa mutane za su iya goyon bayansa bisa kashin kansu, amma ba a matsayin mambobin jam'iyyar ba.

Ita ma jam'iyyar kwaminis ta kasar SACP, dake kawance da jam'iyyar ANC, ta nesanta kanta da shi. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China