in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Zimbabwe ta gayyaci kasashe sama da 40 don sanya ido a zaben kasar
2018-04-10 09:30:44 cri
Gwamnatin kasar Zimbabwe ta gayyaci kasashen duniya 46 a duk fadin duniya ciki har da kasar Sin domin su ziyarci kasar don sanya ido a babban zaben kasar da za'a gudanar a tsakiyar wannan shekara.

Jaridar Herald mallakar gwamnatin kasar ta wallafa wani rahoto a shafinta na yanar gizo dake cewa, bisa ga jerin sunayen masu sanya idon da kasar ta gayyata, wanda ma'aikatar harkokin waje da hada hadar cinikin kasa da kasa ta kasar ta fitar ya nuna cewa, akwai wasu hukumomi na shiyya da nahiyoyi kimanin 15 wadanda kasar ta gayyata don su sanya ido a zaben kasar.

Daga cikin wadanda kasar ta gayyata har da kungiyar tarayyar Turai da kasar Amurka, wadanda suka jima ba su halarci kasar don sanya ido a zaben ba tun a shekarar 2002, a lokacin da dangantakarsu ta yi tsami da kasar bisa zargin da ake yiwa Zimbabwe na take hakkin bil adama.

Goron gayyatar da aka baiwa masu sanya ido daga kasashen waje ya zo ne a daidai lokacin da kasar Zimbabwen ke ci gaba da fadi tashin ganin an gudanar da sahihin zabe mai tsabta wanda shugaban kasar Emmerson Mnangagwa ya ayyana hakan.

A watan jiya ma, wata tawaga daga al'ummar raya ci gaban kasashen kudancin Afrika da wata tawaga daga kungiyar tarayyar Turai sun ziyarci kasar ta Zimbabwe a mabanbantan lokuta, domin duba irin shirye-shiryen da kasar ke yi wajen tunkarar zaben. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China