in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kada Amurka ta yi gudun gara ta fadawa zago
2018-04-06 16:54:36 cri
Dangane da kalaman shugaba Donald Trump na Amurka, na duba yiwuwar kara harajin da yawansa ya kai dala biliyan 100, kan karin wasu hajojin da Sin ke sayarwa Amurka, shafin intanet na jaridar People's Daily ta kasar Sin ya wallafa wani sharhi a yau Jumma'a, mai kunshe da gargadi ga Amurka da kada ta yi gudun gara ta fadawa zago.

Wannan sharhi ya bayyana cewa, game da wannan sauyi da bangaren Amurka ya yi ba zato ba tsammani, jama'a da masana wadanda suka kware a fannin ilmin tattalin arziki, da 'yan majalissun dokokin kasar na jihohi daban daban, sun nuna shakku kan matakan da Donald Trump ya dauka.

Sharhin ya ce matakan dai, baya ga rashin amincewa daga bangaren al'ummar Amurka, sun kuma hadu da adawa daga dukkanin sassan fadin duniya. Idan an kaddamar da yakin cinikayya, tabbas ba wanda zai ci nasara. Kuma yanzu haka bangaren Sin yana aiwatar da matakan mayar da martani kan matakan bisa shirinsa, kuma zai sa bangaren Amurka ya gane ma'anar "Gudun gara a fadawa zago". Kaza lika al'ummar Amurka ma za su gane wanda ya yi musu alkawarin samar da alheri, amma a maimakon haka ya sanya su tunkarar rasa guraben ayyukan yi. (Sanusi Chen)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China