in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kakaki: EU ba ta goyon bayan saba dokokin WTO
2018-04-05 12:46:50 cri
Kakakin kungiyar tarayyar Turai (EU), Daniel Rosario, ya ce, EU ba ta goyon bayan daukar matakan da suka sabawa dokokin hukumar ciniki ta duniya WTO, ya fadawa 'yan jaridu jiya Laraba a birnin Washington cewa, matakin karin harajin kashi 25 bisa 100 a kan kayayyaki kirar kasar Sin wanda bincike ya nuna cewa an fake ne da sashe na 301.

Rosario ya ce, "Muna kira ga bangarorin da abin ya shafa da su tabbatar da ganin an mutunta dokokin hukumar WTO a bangaren hada hadar ciniki na kasa da kasa. Za mu nazarci irin matakan da aka dauka ko sun dace da manufofin hukumar WTO", jami'in ya bayyana hakan ne a yayin da yake amsa tambayoyin da kamfanin dillancin labarai na Xinhua suka yi masa kan wannan batu.

A cewar kakakin, EU ta lura da cewa matakin da Amurka ta dauka mai lamba 301 ya sabawa moriyar kasar Sin, kuma suna ci gaba da binciken da suke yi a kan batun tun a watan Augastan shekarar 2017. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China