in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jakadun EU sun bayyana matsayarsu game da matsayin birnin Kudus
2017-12-09 12:34:13 cri

Jakadun kasashe mambobin Tarayyar Turai a MDD, sun fitar da wata sanarwar hadin gwiwa a jiya Jumma'a, inda suka bayyana rashin amincewarsu da matakin Shugaban Amurka Donald Trump, na ayyana birnin Kudus a matsayin babban birnin Isra'ila. Suna masu kira da a tabbatar da zaman lafiya a yankin gabas ta tsakiya.

Sanarwar da Jakadun Birtaniya da Faransa da Jamus da Italiya da Sweden suka fitar, ta ce ba sa goyon bayan matakin na Amurka da kuma fara shirin mayar da ofishin jakadancin Amurka zuwa birnin Kudus daga Tel Aviv. Inda suka ce matakin ya sabawa kudurorin kwamitin sulhu na MDD, kuma ba zai amfanawa yunkurin wanzar da zaman lafiya a yankin ba.

Sanarwar ta ce dole ne tabbatar da matsayin birnin Kudus ya kasance bisa cimma yarjejeniya tsakanin Isra'ila da Falasdinu.

A cewar jakadun, bisa ka'idojin Tarayyar Turai, matsayar mambobinta ita ce, kasancewar birnin Kudus matsayin babban birnin Isra'ila da Falasdinu. Kuma kafin sannan a wajensu, babu wata kasa dake da iko da birnin. (Fa'iza Msuatpha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China