in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen EU sun cimma daidaito kan takardar shirya shawarwarin ficewar Birtaniya daga kungiyar EU
2017-04-30 12:52:05 cri
A jiya 29 ga wata ne, kungiyar tarayyar Turai EU ta gudanar da taron shugabannin kasashe 27 membobin kungiyar ban da kasar Birtaniya, inda suka tattauna kan batun janyewar kasar Birtaniya daga kungiyar ta EU. Shugaban majalisar zartarwar kungitar Donald Tusk‎ ya bayyana a gun taron manema labaru da aka gudanar bayan taron cewa, kasashen kungiyar 27 sun cimma daidaito kan takardar shirya shawarwarin ficewar Birtaniya daga cikin kungiyar EU.

Bisa takardar da kungiyar EU ta gabatar, an amince da shawarwarin ficewar Birtaniya daga kungiyar EU bisa aya ta 50 dake cikin yarjejeniyar Lisbon da kuma ka'idojin da kungiyar EU za ta bi a yayin shawarwarin. Kana takardar ta jaddada kiyaye kasuwa da matsayin kasashe membobin kungiyar a yayin shawarwarin da sauransu.

A ranar 29 ga watan Maris ne firaministar kasar Birtaniya Theresa May ta mikawa kungiyar EU wasika, inda ta sanar da fara shirin ficewar kasarta daga kungiyar EU. Kasar Birtaniya da kungiyar EU suna da shekaru biyu don kammala shawarwarin ficewar kasar daga kungiyar ta EU. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China