in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya za ta ci gaba da amfani da kashi 14 bisa 100 a matsayin matakin bada rance a kasar
2018-04-05 12:27:53 cri
Gwamnatin Najeriya ta tabbatar da cewa za ta ci gaba da tafiyar da harkokin kudadenta a kan kashi 14 bisa 100 sakamakon rashin tabbas game da sha'anin tattalin arziki da kuma karuwar farashin kayayyaki.

Da yake jawabi ga manema labarai a Abuja, babban birnin kasar, Godwin Emefiele, gwamnan babban bankin kasar (CBN) ya ce, makomar tattalin arzikin kasar na shekarar nan ta 2018 ya kasance cikin kyakkyawan yanayi amma hakan zai ta'allaka ne kan amincewa da kuma aiwatar da kasafin kudin kasar na shekarar 2018 a kan lokaci.

Emefiele, wanda ya gabatar da jawabi a karshen taron kwamitin tsara al'amurran kudin kasar (MPC) na shekarar 2018, ya kara da cewa, ci gaban da tattalin arzikin kasar ya samu ya samo asali ne daga kyautatuwar al'amurran tsaro da aka samu a kasar, da daidaituwar kasuwar masuyar kudaden kasar, da kuma ingancin farashin albarkatun danyen mai a kasuwar duniya.

Ya ce mambobin kwamitin na MPC sun kada kuri'ar amincewa da ci gaba da tafiyar da tsarin kudaden kasar kan matakin da ake amfani da shi a halin yanzu da ma sauran batutuwa da suka shafi harkokin kudade a kasar.

A cewarsa, kwamitin yana da ra'ayin cewa tsaurara matakan zai yi tasiri kan tsarin kudaden kasar game da hawa-hawar farashin kayayyaki wanda kuma zai iya shafar yadda kudaden kasar ke gudana da kuma daidaita kasuwar musayar kudade a kasar. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China