in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rwanda da Najeriya sun rattaba hannu kan yarjejeniyar sararin samaniya
2018-03-27 09:15:34 cri
Gwamnatocin kasashen Rwanda da Najeriya sun rattaba hannu kan yarjejeniya a fannin sararin samaniyan kasashen biyu bayan da kamfanin jirgin saman RwandAir ya yi shawagi a sararin samaniyar Najeriyar.

An dai sanya hannu kan yarjejeniyar ne a Kigali, babban birnin kasar ta Rwandan, wanda Dieu Uwihanganye, karamin ministan sufurin kasar Rwanda, da Hadi Abubakar Sirika, karamin ministan sufuri jiragen saman Najeriya suka rattaba hannu a madadin gwamnatocin kasashen biyu.

Yarjejeniyar ta kunshi batun hadin gwiwa wajen samar da horo da musayar kwararru a fannin sufurin jiragen saman kasashen Rwanda da Najeriya.

Yarjejeniyar za ta kara sadarwa tsakanin kasashen biyu da kuma bunkasa harkokin cinikayya a tsakaninsu, in ji Uwihanganye, bayan da suka kammala sanya hannu kan yarjejeniyar.

Ya ce yarjejeniyar wani tsari ne na cude-ni-in-cude-ka wanda zai hada sassan kasashen biyu wadda ake sa ran zai taimaka wajen bunkasa harkokin hukumomi masu zaman kansu domin amfanawa ci gaban tattalin arziki da zamantakewar al'ummomin kasashen biyu.

A yanzu haka jirgin saman RwandAir ya tashi zuwa birnin Lagos domin tsara yadda za'a fara sufurin daga Rwanda zuwa Abuja a watan Mayun shekara ta 2018. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China