in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wasu tsageru sun kashe mutane 32 a Nijeriya
2018-03-31 12:39:45 cri

Wasu tsageru sun kashe wasu mutanen kauye 32 a jihar Zamfara dake arewa maso yammacin Nijeriya.

Shugaban karamar hukumar Anka Mustapha Gado, wanda ya tabbatar da aukuwar al'amarin, ya ce an binne mutane 32 a ranar Alhamis, ciki har da wata mata da danta, wadanda suka mutu a wani asibiti dake birnin Gusau.

Mustapha Gado, ya ce har yanzu ana bincike don gano wasu gawawwakin a daji, sannan an kara tsaurara matakan tsaro a yankin, sai dai a cewarsa, dukkan al'ummar kauyen sun tsere saboda fargabar kada tsagerun su kuma komawa.

Majiyoyi daga hukumomin taro sun ce tsagerun sun kai hari kauyen Bawan Daji ne a ranar Talata da ta gabata, bayan wasu mutanen yankin sun gudanar da taro don tattauna matakan da za su dauka kan tsagerun a lokacin daminar bana.

Majiyar ta kara da cewa, tun da farko dai, tsagerun sun yi barazanar cewa babu wani aikin gona da zai gudana a yankin a bana. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China