in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fara gina wata babbar tashar jiragen ruwa a Najeriya
2018-03-30 16:20:34 cri

An kaddamar da aikin gina tashar jiragen ruwa cikin ruwa mai zurfi ta Lekki a jihar Legas ta kasar Najeriya a jiya Alhamis. Bayan kammala aikin, tashar za ta zama irinta mafi girma a yankin kudu da hamadar Sahara. Tashar kuma za ta kawo karshen tarihin kasar Najeriya na rashin samun tashar jirgin ruwa da ke samun ruwa mai zurfi.

Mataimakin shugaban kasar Najeriya Yemi Osinbajo da ya halarci bikin kaddamar da aikin, ya ce wannan sabuwar tashar jiragen ruwa za ta haifar da karin moriya ga yankin ciniki cikin 'yanci na Lekki. Yayin da a nasa bangare, Rotimi Amaechi, ministan sufuri na kasar, ya ce wannan tasha za ta taimaka wajen tabbatar da matsayin Najeriya na cibiyar zirga-zirgar jiragen ruwa a yankin da take ciki.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China