in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Xi Jinping ya taya Abdel-Fattah al-Sisi murnar sake zama shugaban Masar
2018-04-03 11:10:16 cri
A jiya Litinin, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya mika sakon taya murna ga shugaban kasar Masar Abdel-Fattah al-Sisi don sake zama shugaban kasar ta Masar a karo na biyu.

A cikin sakon, Xi Jinping ya bayyana cewa, ana sada zumunta a tsakanin Sin da Masar a dogon lokaci. A shekarun baya baya nan, Xi da shugaba al-Sisi sun kiyaye mu'amala da juna, da kara yin imani da juna a fannin siyasa, da inganta hadin gwiwar dake tsakanin kasashen biyu, da kara yin mu'amalar al'adu da juna, ta haka jama'ar kasashen biyu suna sada zumunta sosai, shugaba Xi yana matukar farin ciki da ganin hakan. Yana fatan kasar Masar za ta kara samun babban ci gaba bisa hanyar dake dace da yanayin kasar a karkashin jagorancin shugaba al-Sisi. Kana ya dora muhimmanci sosai ga dangantakar dake tsakanin Sin da Masar, yana son yin kokari tare da shugaba al-Sisi wajen sa kaimi ga raya dangantakar abokantaka bisa manyan tsare-tsare a dukkan fannoni a tsakanin kasashen biyu zuwa wani sabon mataki don amfanawa jama'arsu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China