Wata sanarwar daga ofishin sashen siyasa na kwamitin kolin JKS, ta bayyana cewa akwai jan aiki game da yakin da kasar Sin take yi da fatara. Sanarwar ta ce ya zama wajibi a kara kaimi domin cimma nasarar da aka sanya gaba.
An dai fidda wannan sanarwa ne a Jumma'ar nan, bayan taron tattauna batutuwan da suka jibanci yaki ta talauci, wanda jami'an sashen siyasa na kwamitin kolin JKS suka gudanar, karkashin jagorancin shugaba Xi Jinping, wanda shi ne kuma babban sakataren kwamitin kolin JKS.(Saminu Alhassan)