in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriyar ta horar da malamai 300 dabarun sanya nutsuwa a zukata masu fama da tashin hankali
2018-03-20 09:50:30 cri
A ranar Litinin gwamnatin Najeriya ta fara shirin horas da malaman makarantun firamare su 300 kan dabarun kwantar da hankula da cusa nutsuwa a zukatan masu fama da tashin hankali a yankin jihar Adamawa dake shiyyar arewa maso gabashin kasar.

Shirin bada horo na mako guda, an tsara shi ne da nufin tallafawa iyaye da yara 'yan makaranta wadanda rikicin 'yan ta da kayar baya ya shafa.

Shugaban kwamitin ba da tallafi na ofishin shugaban kasa a shiyyar arewa maso gabas (PCNI) Theophilus Danjuma, ya ce wannan shirin ya zama dole a kaddamar da shi sakamakon matsalar koma bayan da yankin ya fada ciki musamman ta fuskar ilmi da tattalin arziki. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China