in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Iran ta yi watsi da rahoton MDD game da kare hakkin dan adam da cewa ba abin amicewa ba ne
2018-03-26 10:36:42 cri
Ma'aikatar harkokin wajen Iran ta yi watsi da rahoton hukumar kare hakkin dan adama ta MDD wato (UNHRC) wanda ta fitar kan zargin Iran game da batun take hakkin bil adama na baya bayan nan.

Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen Iran Bahram Qasemi, ya karyata rahoton a lokacin taron kwamitin UNHRC na baya bayan nan a Geneva, wanda kwamitin MDDr ya bukaci a tsawaita wa'adin shirin musamman na sanya ido kan take hakkin dan adama a kasar Iran din zuwa tsawon shekara guda.

Qasemi ya ce, a ra'ayinsu, tsawaita shirin rahoton kare hakkin dan adam har na tsawon shekara guda abu ne da bai dace ba kuma bai kamata ba. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China