in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilan kasashen turai sun jaddada amincewa da yarjejeniyar nukiliyar Iran
2018-01-12 10:28:21 cri
Manyan kusoshin kasashen Turai, sun jaddada goyon bayan su ga yarjejeniyar nukiliyar kasar Iran da aka cimma a shekarar 2015.

A jiya Alhamis ne dai jagoran ofishin dake lura da harkokin kasashen waje na kungiyar tarayya Turai EU Federica Mogherini, da ministocin harkokin wajen kasashen Faransa, da Jamus, da Birtaniya, suka gana da takwaran su na kasar Iran Mohammad Javad Zarif, inda suka bayyana masa gamsuwar su game da yadda ake aiwatar da wannan yarjejeniya.

Hakan dai na zuwa ne yayin da ake dakon matakin da shugaban Amurka Donald Trump zai dauka game kakabawa Iran din takunkumi.

A ranar 13 ga watan Oktobar da ya shude ne dai shugaba Trump ya bayyana rashin gamsuwar sa da yadda Iran ke aiwatar da waccan yarjejeniya. To sai dai kuma cikin watanni 2 da suka gabata, majalissar dokokin Amurka ba ta zartas da wani kuduri game da kakabawa Iran din takunkumi ba. Kuma hakan na nufin shugaban Amurkan, na da ikon yanke shawarar daukar matakin kakabawa Iran din sabon takunkumin makamashi, ko kuma ya ayyana wani matakin na daban.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China