in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta bukaci a gudanar da sauye sauyen MDD bisa gaskiya da adalci a guji sanya siyasa
2018-03-20 11:05:13 cri
Kasar Sin ta yi kira ga dukkan bangarorin da abin ya shafa da su gudanar da harkokinsu ba tare da rufa rufa ba bisa adalci, kuma ba tare da sanya siyasa ba a lokacin gudanar da sauye-sauye na lokaci-lokaci da ake gudanarwa wato (UPR), karkashin shirin kare hakkin dan adam na MDD, kamar yadda jami'in diplomasiyyar Sin ya bayyana.

Sakamakon irin muhimmancin da take bayarwa ga sauye-sauyen na UPR, kasar Sin ta bayyana cewa yin hadin gwiwa abu ne mai matukar muhimmanci da zai taimaka wajen aiwatar da shawarwarin da za su taimakawa kasashen duniya masu tasowa, in ji jami'in diplomasiyyar na Sin.

Da yammacin ranar Litinin ne kwamitin kare hakkin bil adama na MDD ya gudanar da babbar muhawara game da yin sauye-sauye a tsarin na UPR, inda masu gabatar da kasidu suka nuna cewa yin gyare-gyaren wata babbar nasara ce, kasancewar batu ne da ya shafi aiwatar da tsarin a aikace, kana ya kasance a matsayin wata dama ta yin tsokaci kan irin nasarorin da aka cimma da kuma kalubalolin da dukkan kasashe ke fuskanta wajen aiwatar da muhimman batutuwan da suka shafi kare hakkin dan adam.

Mafi yawan kasashen duniya sun rungumi tsarin na UPR, kasancewarsa wani tsari ne da ake sake yin nazari kansa a duk bayan shekaru 4, don nazartar yanayin halin da hakkin dan adam ke ciki, da nazartar al'amurra da suka shafi wannan batu, da sanya ido kan irin nasarorin da kasashen duniya suka cimma a wannan fanni. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China