in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An gaza cimma matsaya a taron kwamitin sulhun MDD game da tsagaita bude wuta a Syria
2018-02-23 10:46:32 cri
A ranar Alhamis kwamitin sulhun MDD ya gudanar da taron tattaunawa game da halin da ake ciki na tashin hankalin dake addabar yankin gabashin Ghouta na kasar Syria, sai dai ba'a samu nasarar cimma matsaya ba game da bukatar da aka mika na neman tsagaita bude wuta na kwanaki 30 a yankin mai fama da rikici.

Kwamitin MDDr yana la'akari da daftarin wanda kasashen Kuwait da Sweden suka tsara, wanda ya bukaci a tsagaita bude wuta daga dukkanin bangarorin dake yaki da juna a duk fadin kasar ta Syria in banda dakarun sojin dake yakar kungiyar IS, da al Qaeda da al Nusra Front, har na tsawon kwanaki 30 domin a samu damar shigar da kayayyakin jin kai da masu ba da agajin kiwon lafiya a yankunan kasar.

Jakadan kasar Sweden a MDD Olof Skoog, ya bayyana cewa, yana fata kwamitin sulhun MDDr zai kada kuri'a kan kudurin a ranar Alhamis. Sai dai jakadan kasar Rasha a MDDr Vassily Nebenzia ya ce, yana fata za'a yi wasu gyare gyare kan kudurin domin ya kasance mai inganci.

A cewar Nebenzia, babu wata matsaya da aka cimma a zaman kwamitin game da batun tsagaita bude wuta, a yayin da tashin hankali ke sake tsakananta a kasar sakamakon karuwar kaddamar da hare hare daga 'yan ta'adda.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China