in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Iyayen 'yan matan da aka sace a Nijeriya sun gudanar da bikin ranar Mata ta duniya cikin kunci
2018-03-09 09:16:44 cri
A karon farko, wasu daga cikin iyayen 'yan matan 110 na sakandaren Dapchi da aka sace, sun taru a Abuja, fadar mulkin kasar domin bayyana bakin cikinsu.

A daidai lokacin da ake bikin ranar mata ta duniya a jiya Alhamis, iyayen sun yi tattaki cikin lumana, domin tunatarwa gwamnatin Nijeriya irin kaddarar da ta aukawa 'ya'yansu a ranar 19 ga watan da ya gabata, lokacin da Kungiyar Bokon Haram ta farwa kwalejin 'yan mata ta Dapchi tare da dauke a kalla 'yan mata 110.

Taken ranar a bana shi ne 'matsa kaimi don samun ci gaba'. Sai dai iyayen sun ce babu yuwar samun wata ci gaba a rayuwarsu, muddun 'ya'yansu ba su dawo nan kusa cikin koshin lafiya ba.

Hukumomin a garin na Dapchi sun dauko malamai a kalla 300, inda suke addu'a a kullum domin neman dawowar 'yan matan cikin koshin lafiya.

Dan majalisa mai wakiltar Dapchi da makotan garuruwa Goni Bukar, ya shaidawa majalisar wakilan kasar cewa, addu'ar ta musammam za ta ci gaba har zuwa lokacin da 'yan matan za su dawo. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China