in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Boko Haram ta kashe jami'an 'yan sanda 10 yayin harin da ta kai arewa maso gabashin Nijeriya
2018-03-09 09:11:06 cri
Rundunar 'yan sandan jihar Borno dake arewa maso gabashin Nijeriya, ta tabbatar da mutuwar jami'anta 4 da sojoji 6, yayin harin da kungiyar Boko Haram ta kai garin Rann na jihar.

Kwamishinan 'yan sandan jihar Damian Chukwu, ya shaidawa manema labarai a Maiduguri babban birnin jihar cewa, 'yan sandan na cikin shirin yaki da ta'addanci domin dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali da aka tura yankuna daban daban.

Damian Chukwu wanda ya ce sama da 'yan sanda 500 ne ke aiki cikin shirin rundunar soji mai taken 'Operation Lafiya Dole', ya jadadda kudurin rundunar na yaki da ta'addanci.

Shi ma ofishin dake kula da harkokin jin kai na MDD, ya ce an kashe jami'an bada agaji 3, yayin da ta ayyana batar wata ma'aikaciyar jinya yayin harin na Rann da aka kai ranar 1 ga wannan wata.

Hukumar ta ce jami'an na aikin bada agaji ne ga 'yan gudun hijira sama da 50,000 da suka tserewa gidajensu saboda tashin hankalin da yanki ke fama da shi.

Har ila yau, Damian Chukwu ya ce an tura 'yan sanda makarantun gwamnati dake jihar domin inganta taro. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China