Kwayoyin cutar mai saurin kisa ta yadu ne a jahohin kasar 18, tun bayan da aka samu rahoton bullar cutar a cikin sabuwar shekara. Kimanin mutane 2,845 da ake kyautata zaton sun kusance wadan da suka kamu da cutar ne aka sanyawa ido a fadi kasar, kamar yadda hukumar ta WHO ta rawaito daga hukumar magance bazuwar cutuka ta kasar (NCDC).(Ahmad Fagam)