in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Taron majalisar NPC ya tabbatar da mambobin majalisar gudanarwar kasar Sin
2018-03-19 11:15:11 cri

An tabbatar da mambobin majalisar gudanarwar kasar Sin ta hanyar jefa kuri'a a yau Litinin, yayin taron majalisar wakilan jama'ar kasar Sin NPC, inda aka zabi Han Zheng da Sun Chunlan da Hu Chunhua da Liu He a matsayin mataimakan firaministan kasar Sin, yayin da Wei Fenghe da Wang Yong da Wang Yi da Xiao Jie da Zhao Kezhi za su kasance mambobin majalisar gudanarwar kasar.

Bisa sunayen da firaministan majalisar gudanarwar kasar Sin Li Keqiang ya gabatar, an kuma jefa kuri'a don nada ministoci da shugabannin kwamitoci da gwamnan babban bankin kasar Sin da shugaban hukumar binciken kudi ta kasar, gami da babban sakataren majalisar gudanarwar kasar.

Bugu da kari, ta hanyar jefa kuri'a, aka zartas da sunayen shugabannin kwamitocin majalisar NPC, da mataimakan shugabannin da ma mambobin majalisar.

Har ila yau, yayin zaman na yau, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya ba da umurnin nada mambobin majalisar gudanarwar kasar bisa kudurin da taron NPC ya tsayar.

Bayan kammala ajandu daban-daban na cikakken zama taron NPC na yau, mataimakan firaminista da mambobin majalisar gudanarwar kasar sun yi rantuwar kama aiki a gaban kundin tsarin mulkin kasar Sin. (Kande Gao)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China