in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Xi Jinping ya lashe zaben shugaban kasar Sin
2018-03-17 10:54:48 cri

Da safiyar yau Asabar agogon Beijing ne aka zabi Xi Jinping a matsayin shugaban jamhuriyar jama'ar kasar Sin, kuma shugaban kwamitin tsakiya na aikin soja na jamhuriyar jama'ar kasar.

An zabi shugaban ne yayin cikakken zaman taro karo na biyar, cikin zagayen farko na taron majalisar wakilan jama'ar kasar Sin karo na 13 a nan birnin Beijing.

Haka kuma, an zabi Li Zhanshu a matsayin shugaban zaunannen kwamitin majalisar wakilan jama'ar kasar Sin karo na 13 da kuma Wang Qishan a matsayin mataimakin shugaban jamhuriyar jama'ar kasar Sin.

Bayan cikakken zaman taron karo na biyar, an yi bikin rantsuwa da kundin tsarin mulkin kasar. Kuma wannan shi ne karon farko da shugabannin kasar Sin suka yi rantsuwa da kundin tsarin mulkin kasa a wajen taron majalisar wakilan jama'ar kasar, tun bayan fara aiwatar da tsarin rantsuwa da kundin tsarin mulkin kasar Sin. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China