in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Dan takarar jam'iyya mai mulkin Saliyo ne ke kan gaba a zaben shugaban kasar
2018-03-11 13:22:58 cri
Shugaban hukumar zaben kasar Saliyo NEC N'Ali Koroma, ya sanar a jiya Asabar kashi 25 bisa 100 na samakon farko na zaben shugaban kasar wanda aka jefa kuri'un a ranar 7 ga watan Maris.

Dan takarar shugabancin kasar na jam'iyyar APC mai mulkin kasar shi ne ke kan gaba da kashi 44.6 bisa 100, sai kuma dan takarar babban jam'iyyar adawar kasar SPP wanda ke bi masa baya da kashi 42 bisa 100. Yayin da dan takarar shugabancin kasar na jam'iyyar NGC yake a matsayi na 3 da kashi 6.6 bisa 100 na yawan kuri'un da aka kada.

A cewar shugaban hukumar ta NEC, a halin yanzu, kashi 25 bisa 100 na sakamakon zaben ne aka sanar, kuma ba shi ne cikakken sakamakon zaben ba.

Ya kara da cewa, a nan gaba za su sanar da kashi 50 bisa 100 na sakamakon zaben kafin karshen wannan rana ta yau.

Sama da mutane miliyan 3 ne suka kada kuri'unsu a zaben inda aka jefa kuri'un domin zabar sabon shugaban kasa da 'yan majisar dokokin kasar da na majalisun kananan hukumomi tun a ranar 7 ga watan Maris. (Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China