in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
WHO ta yi gargadin yaduwar cututtuka a Saliyo bayan iftila'in zaftarewar laka
2017-08-22 09:37:51 cri
Hukumar lafiya ta duniya WHO, ta yi gargadin cewa, akwai yiwuwar yaduwar wasu cututtuka dake akwai a Saliyo, bayan zaftarewar laka da ta auku a makon da ya gabata, iftila'in da ya yi sanadin mutuwar mutane 500.

WHO ta kara da cewa, la'akari da lalacewar hanyoyin ruwa da kayayyakin tsaftace muhalli, mazauna yankunan da iftila'in ya shafa a kasar dake yammacin Afrika na cikin hadarin fuskantar barkewar wasu cututtukan da da ma akwai su a kasar, wadanda suka hada da zazzabin cizon sauro da cututtukan da kan haifar da amai da gudawa da suka hada da zazzabin gudanawa da kwalara.

Barkewar cutar kwalara da aka samu a kasar a baya-bayan nan ya auku ne a shekarar 2012.

A yanzu haka, WHO na aiki da hukumomin lafiya dake kasar domin kara kaimi wajen daukar matakan kariya da kuma tunkarar barkewar cututtuka. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China