Taron na yini biyu da ake yi a Kigali babban birnin kasar Rwanda, na gudana ne gabanin taron AU kan yankin na cinikayya da zai gudana daga ranar 17 zuwa 21 ga watan nan da muke ciki a birnin na Kigali.
A cewar ministan ciniki na Rwanda Vincent Munyeshyaka, abu ne mai muhimmanci a gaggauta cimma yarjejeniya game da yankin, domin tabbatar da burin nahiyar na samar da kasuwar bai daya ga kasashenta. (Fa'iza Msutapha)