in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
AU ta goyi bayan saukaka zirga-zirgar jama'a tsakanin nahiyar
2018-02-13 09:57:16 cri
Mataimakin wakilin shugaban hukumar zartarwas kungiyar tarayyar Afirka na musamman mai kula da kasar Somaliya Simon Mulongo, ya bayyana cewa, kungiyar tana goyon bayan zirga-zirgar al'ummar nahiyar ba tare da wani shamaki ba.

Simon wanda ya bayyana hakan a jiya Litinin a Mogadishu, yayin da yake jawabi yayin cin abincin rana a taron tuntubar juna na kwanaki 4 da kungiyar IGAD ta shirya game da yadda za a saukaka zirga-zirga tsakanin al'ummomin nahiyar ya ce, kungiyar tana hada kai da hukumomin tattalin arziki da ragowar masu ruwa da tsaki dake yankin don fito da matakan da za su tabbatar da ganin an cimma wannan buri.

Mulongo ya yi maraba da matakin na IGAD, yana mai cewa, zai taimaka wajen bunkasa harkokin cinikayya da hade tattalin arzikin yankin waje guda

Yanzu haka dai, kungiyar mai mambobi 8 tana kokarin saukaka zirga-zirga tsakanin al'ummomin kasashen nahiyar ta yadda za su rika yin cinikayya a yankin da ya kai fadin murabba'in kilomita miliyan 5.2 ba tare da wani shinge ba.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China